Ban hana 'yan Shi'a yin shi'arsu ba - Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce umarnin da kotu ta bayar na dakatar da kungiyar IMN bai hana mabiya Shi'a su gudanar da addininsu ba a kasar.
Kalaman shugaban na zuwa ne bayan hukuncin wata kotu a Abuja, ranar Juma'a, da ya bayar da umarnin haramta Kungiyar IMN ta mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky kamar yadda gwamnati ta nema.
Bayanan kotun sun nuna cewa gwamnati ta nemi a haramta kungiyar ta IMN bayan ayyana ta a matsayin ta 'yan ta'adda, inda ta zarge ta da haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.
Mai magana da yawun kungiyar Ibrahim Musa ya yi watsi da zargin cewa suna tayar da husuma, sannan ya shaida wa BBC lauyoyi da jagororinsu na nazari kan umarnin kotun domin fitar da matsaya.
Tashin hankali ya kazanta a baya-bayan nan tsakanin jami'an tsaro da magoya bayan kungiyar, wadanda ke zanga-zanga akai-akai tun bayan tsare shugabansu da gwamnati ta yi a shekarar 2015.
Sai dai mai magana da yawun Shugaba Buhari, Malam Garba Shehu, ya shaida wa BBC cewa za a aiwatar da wannan hukunci na kotu domin haramta kungiyar ta IMN, amma ya ce hakan ba yana nufin haramta Shi'a ba.
"Akwai miliyoyin 'yan Shi'a a kasar nan wadanda suke zaune lafiya kuma gwamnati ba ta da matsala da su, ba wanda zai tsangwama musu kaa yadda suke harkokinsu... Ba mu hana kowa yin Shi'arsa ba," in ji malam Garba.
Ya kara da cewa gwamnati ta nemi wannan hukunci ne domin "haramta ayyukan kungiyar IMN karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaky".


Copied on BBCHAUSA.COM

Post a Comment

0 Comments