Gwamnatin tarayya ta fitar da ranar da za a fara WEAC

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanya ranar fara jarrabawar kammala makarantar sakandare ta WAEC ta shekarar 2020.
Jaridar Punch ta ruwaito cewar karamin Ministan Ilimi na Najeriya Emeka Nwajiuba ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wajen taron kwamitin shugaban kasa na yaki da COVID-19 a Abuja, babban birnin kasar.
Ya ce za a yi jarrabawar ne daga ranar 4 ga watan Agusta zuwa 5 ga watan Satumban 2020.
Nwajiuba ya ce, “Za a fara jarrabawar daga 4 ga watan Agusta zuwa 5 ga Satumba. Don haka iyaye ku aje hakan a ranku.
''Mun yi iyakar yin mu kuma mun tattauna da wakilanmu a WAEC yau da rana, muyn tabbatar da ranakun cewa za a yi jarrabawar ne daga ranar 4 ga watan Agusta zuwa 5 ga Satumba.
“Daga gobe, za mu daddale da masu ruwa da tsaki a harkar, duk za su halarci taron na gobe.

Copied BBC HAUSA

Post a Comment

0 Comments